GONI: MAJALLAR ILIMIN ALKUR’ANI

Cibiyar Nazari akan Alkur’ani da ke Jami’ar Bayero ta Kano, ta kuduri aniyar wallafa Majalla da harshen Hausa da kuma Ajami, wadda musamman za ta dukufa wajen hidima ga ilimin Alkur’ani. Majallar za ta gabatar da bincike da bayanai da labarai da suka shafi fannonin iliman Alkur’ani. Manufar Majallar ita ce samar da wani dandali da malaman Alkur’ani za su baje kolin iliman Alkur’ani domin kusantar da fahimtarsa ga al’umma.

Majallar za ta zakulo abubuwan alfaharinmu na tarihin iliman Alkur’ani a wannan kasa, musamman fannonin iliman Kur'ani da malaman wannan kasa suka yi fice a kai. Don haka za ta fuskantar da bayanai akan kafuwar makarantun tsangaya da yaduwar ilimin Alkur’ani da tarihin fitattun Alarammomi da Gwanaye na da can da na yanzu da yanayin tsare-tsarensu wajen habaka koyon karatun Alkur’ani. Majallar za ta kuma yi kokarin fayyace bayanai na malamai da masana akan hanyoyin da suka dace a bi domin habaka makarantun Alkur’ani da tsangayu da inganta manhajarsu domin dacewa da muhimman bukatun al’ummar Musulmi a yau.

Majallar Al-Goni za ta kunshi bayanai da labarai na ayyukan Cibiyar bincike akan Alkur’ani da sauran cibiyoyi da makarantun Alkur’ani.

Ga Ajamin:

ثِيبِيَرْ نَزَرِنْ أَلْقُرْآنِے مَيْ غِرْمَا، جَامِئَرْ بَايَرُوْ، كَنُوْ تَا قُدُرِ أَنِيَرْ وَلَّفَ مَجَلاَّ دَ هَرْشٜنْ هَوْسَا دَ كُمَ أَجَمِ، مَيْ سُونَا "أَلْغَونِے"، وَدَّ مُسَمَّنْ زَا تَ دُقُفَ وَجٜنْ يِنْ هِدِمَا غَ إِلِـمنْ أَلْقُرْآنِے مَيْ غِرْمَا دَ ڟَنْغَيُنْسَ دَ كُمَ إِنْغَنْتَ مَنْهَجَرْسُ دُوْمِنْ دَاثٜىٰوَا دَ مُهِمَّنْ بُقَاتُنْ أَلْأُمَّرْ مُسُلْمِے أَ يَوْ.


مُجَلَّرْ أَلْغَونِے، زَا تَ رِقَ غَبَاتَرْ دَ بِنْثِكٜىٰ دَ بَيَانَيْ دَ لاَبَارَيْ نَ يَوْ دَ كُلُّمْ، وَطَنْدَ سُكَ شَا فِ فَنُّوْنِنْ إِلِـمنْ أَلْقُرْآنِے مَيْ غِرْمَا دَ كُمَ أُوَا أُبَا بَيَانَيْ كَنْ أَيُّكَنْ ثِيبِيَا، سَنَّنْ كُمَ دَ بَيَانَيْ كَنْ تَكَورُوْرِنْتَ ثِيبِيُوْيِنْ أَلْقُرْآنِے دَ كُمَ مَكَرَنْتُنْسَ غَ أَلْأُمَّا.


مَنُفَرْ وَنَّنْ مُجَلاَّ إِتَ ثٜىٰ سَامَرْ وَ دَ مَالَـمَيْ دَ طَالِبَنْ أَلْقُرْآنِے مَيْ غِرْمَا وَنِ دَنْدَلِے وَنْدَ زَا سُ رِقَ بَجٜىٰ كُوْلِنْسُ نَ تَتَّوْنَاوَا دَنْغَنٜىٰ دَ إِلِـمِنْ دَ أَلْقُرْآنِے مَيْ غِرْمَا دُوْمِنْ كُسَنْتَرْ دَ فَهِنْتَرْسَ غَ أَلْأُمَّا.